Isa ga babban shafi
Wasanni

Real Madrid ta soma tuntubar Mourinho

Rahotanni daga Spain sun ce Real Madrid ta soma tuntubar tsohon kocinta Jose Mourinho domin sake kulla yarjejeniya da shi, don maye gurbin Zinaden Zidane.

Mai horas da kungiyar Real Madrid Zinedine Zidane.
Mai horas da kungiyar Real Madrid Zinedine Zidane. REUTERS/Juan Medina
Talla

Labarin da jaridar El Chiringuito ta rawaito, ya zo ne kwana guda bayan da Zidane ya ce yawaita sukar salon horaswarsa da ake yi gami da yada jita jitar Mourinho zai maye gurbinsa yana ci masa tuwo a kwarya.

Tun bayan sallamarsa da Manchester United ta yi a watan Disambar bara, zuwa yanzu Mourinho yayi watsi da tayin kulla yarjejeniya da kungiyoyin da suka hada da Benfica da kuma Lyon.

A karshen makon da ya kare, Real Madrid ta sha kaye a hannun Real Mallorca da kwallon 1 mai ban haushi, abinda ya haifar da shakku kan dorewar aikin Zidane, wanda tun bayan sake karbar jagorancin kungiyar ta Madrid, al’amuranta suka gaza komawa kamar lokacin da ya jagorance ta wajen lashe kofunan gasar zakarun Turai uku a jere.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.