Isa ga babban shafi
Wasanni

Bale ya gargadi Real Madrid kan lafiyarsa

Gareth Bale na Wales ya bukaci Real Madrid kar ta kuskura ta wallafa bayanan lafiyarsa, saboda yana da damar kin amincewa da wallafa bayanan kamar yadda dokar Spain ta zayyana.

Gareth Bale
Gareth Bale REUTERS/Javier Barbancho
Talla

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da jaridar Marca ta ce, Kungiyar Kwallon Kafa ta Shanghai Shenhua ta sake yunkurawa domin sayen Bale daga Real Madrid.

Ko a ranar Litinin, sai da dan wasan ya yi balaguro zuwa birnin Laondon domin ganawa da dillalinsa a daidai lokacin da ake ganin makomarsa ba ta da tabbas a Real Madrid.

Kodayake Real Madrid ta ce, Bale ya ziyarci London ne saboda wasu dalilai na kashin kansa.

Kiris ya rage dan wasan ya koma China a kakar da ta gabata domin ci gaba da taka leda amma Real Madrid ta haddasa tarnakin da ya hana shi raba gari daita a wancan lokacin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.