Wasanmu da Manchester City wata dama ce a gare mu- Solskjaer
Kocin Manchester United, Ole Gunnar Solskjaer ya ce, karan-battar da za su yi da Manchester City a gobe Asabar, wata dama ce da za su yi amfani da ita wajen sauya shakkun da ake da shi kan kungiyar zuwa kwarin guiwa.
Wallafawa ranar:
Duk da cewa kungiyar ta Manchester United ta fara kakar bana mafi muni tun shekarar 1988, amma ta yi nasarar casa Tottenham a tsakiyar makon nan, inda kuma ta haura matsayi na shida a teburin gasar firimiyar Ingila.
Kodayake Solskjaer ya ce, karawarsu da Manchester City za ta yi zafi, amma suna bukatar ci gaba da nuna karsashi a cewarsa.
Kocin Manchester City shi ma ya ce, za su dauki wasan da muhimmanci duk da tazarar maki 11 da suka bai wa Manchester United a teburi.
Kungiyoyin biyu sun dade suna hamayya da juna a fagen tamaula.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu