Isa ga babban shafi
Wasanni-Olympics-coronavirus

Tokyo 2020: Coronavirus na neman kawo nakasu ga shirin China

Annobar coronavirus ta kawo cikas ga shirin fafatawa a gasar Olympics da ‘yan wasan guje – guje da tsalle – tsalle na kasar China ke yi, inda ta tilasta musu tsallaka wasu wasannin neman cancanta, sannan aka killace su wajen atisaye, wani lokacin ma sai sun sanya mayanin fuska.

Wasu mutane a China sanye da mayanin fuska don gudun harbuwa da Coronavirus.
Wasu mutane a China sanye da mayanin fuska don gudun harbuwa da Coronavirus. REUTERS/Aly Song
Talla

Masu shirya wasanni dai sun yi ittifakin cewa wannan annobar da ta bulla daga birnin Wuhan, ta kuma kashe mutane sama da 2100 ba za ta kawo nakasu ga wannan gasa da suke shirin tafiya ba.

Sai dai ana ganin mai yiwuwa ta yi mummunan tasiri ga tawagar kasar China, wadda a gasar Rio ta 2016 ta kunshi ‘yan wasa 416, kuma ke cikin ukun farko a duk gasanin da aka yi a wannan karnin.

Babu wanda ya kamu da wannan cuta dai a cikin tawagar ta kasar China, amma bullar annobar ta zo a wani lokaci mai mahimanci a shirin da suke na zuwa gasar da za a fara ranar 24 ga watan Yulin wannan shekarar.

Wani misali a nan dai shine, tawagar kwallon kafar mata ta China, ta koma yin atisaye a farfajiyar wani otel, wato Brisbane Otel, bayan an killace su gabannin wasan neman cancantar fafatawa a Olympics din.

China dai na fata takwarorinta za su bude kofofinsu ga ‘yan wasanta a yayin wasannin neman tikiti, inda tuni wasu kasashe, ciki har da Australia suka tsaurara bincike kan ‘yan China da ke shigowa kasashensu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.