Cote d’ivoire
Kofi Anan ya yi Allah waddai da matakin Gbagbo
Tsohon Sakatare Janar na Majalisar Dunkin Duniya, Kofi Annan, ya bayyana matakin da shugaba Laurent Gbagbo ya dauka, na cigaba da zama kan karagar mulki, bayan faduwa zabe a matsayin abun kunya.A wata hira da yayi da Radio Faransa, Annan ya bayyana bacin ransa kan halin da Cote d’Ivoire ta tsinci kanta a ciki."Abin kunya ganin inda lamarin ya kai, na dauka wannan karon Cote d’Ivoire ta samu damar ficewa daga wannan hali, wannan ya dada bayyana munanan halayen shugaba Gbagbo, duk wani mai sa ido ya san ya fadi zaben, saboda haka ya dace ya mika mulki".
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: