Libya
Kungiyar Tsaro ta NATO ta yi watsi da zargin gwamnatin Libya
Kawancen Kungiyar Tsaron Tekun Arewacin Atlantica ta NATO-OTAN, ta yi fatali da zargin da Shugaban Libya Muammar Gaddafi ya yi na cewa tana aiwatar da laifukan yaki.A cikin wata sanarwa kakakin kungiyar Oana Lungescu, ya bayyana kalaman PM kasar ta Libya Baghdadi Mahmudi, a matsayin neman fakewa da guzuma domin a harbi karsana, domin kowa yasan yadda NATO ke aikin tabbatar da kare fararen hula na kasar.Kungiyar ta ci gaba da kai hare haren karya lagon Shugaba Gaddafi, wanda ke fuskantan boyen al’umma abunda ya haifar da tawaye a cikin kasar.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: