Isa ga babban shafi
World-Libya

Shugabannin Duniya suna ganin karshen Gaddafi shi ne karshen Mulkin kama-karya

Shugabannin kasashen duniya sun yi jinjina ga mutuwar tsohon shugaban Libya Muammar Gaddafi, tare da danganta karshensa a matsayin karshen mulkin kama-karya tare da fatar ganin gina sabuwar kasar Libya.Bayan sanar da mutuwar Gaddafi Shugaban kasar Amurka Barrack Obama yace mutuwar shugaban ita ce karshen babin bakin-ciki a kasar Libya, tare da kiran hada kan ‘yan tawaye wajen kokarin gina sabuwar Libya.

Murnan mutuwar Gaddafi a Tripoli
Murnan mutuwar Gaddafi a Tripoli AFP/Mahmud Turkia
Talla

01:15

Rehoton cafke Gaddafi

Fira Ministan Birtaniya David Cameron yace mutuwar Gaddafi wata dama ce wajen girka Demokradiyya a Libya bayan bayyana wadanda suka mutu karkashin tsohon shugaban tun a harin Lockerbie a shekarar 1988.

 

Shugaban Faransa Nicolas Sarkozy yace al’ummar Libya sun yi yakin neman ‘yanci daga gwamnatin danniya bayan kwashe shekaru 40 tana mulkinsu.

01:36

Martanin Shugabannin kasashen Duniya

Faransa da Amurka da Birtaniya sune kasashen da suka jagoranci yaki a libya ta mafani da NATO da suka kaddamar da hare hare kusan 1,000 tun a watan Mayu.

Kasar China da ke adawa da NATO ta yi fatar ganin an girka sabuwar Libya cikin lokaci kalilan domin kare al’umma da ci gabansu.

01:21

Tarihin Gaddafi

Sai dai kuma Shugaban Venuzeula Hugo Chavez yace kisan Gaddafi kisan gilla ne, a cewarsa zasu ci gaba da tuna Gaddafi a matsayin jarumi wanda ya mutu da kishin kasarsa.

A kasar Itali da ta mulki kasar Libya, Fira Ministan kasar Silvio Berlusconi yace yanzu yaki ya kawo karshe tare da fatar zaman lafiya a Libya bayan kawo karshen Gaddafi

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.