Isa ga babban shafi
AU

AU ta tsawaita shugabancin Jean Ping har zuwa watan Yuni

Kungiyar kasashen Afrika ta tsawaita wa’adin babban Jami’inta Jean Ping har zuwa wani zaman Taron da za’a gudanar a Malawi a watan Yuni bayan gudanar da zaben da ya fuskanci hamayya daga Nkosazana Dlamini-Zuma ‘Yar kasar Afrika ta kudu.

Jean Ping da abokiyar hamayyar shi Dlamini Zuma
Jean Ping da abokiyar hamayyar shi Dlamini Zuma AFP
Talla

Shugabar kasar Benin kuma shugaban kungiyar Thomas Boni Yayi, yace sun yanke hukuncin tsawaita wa’adin shugabancin Mista Ping ne har zuwa wani zaman taron.

Zaben shugabannin kungiyar ne ya mamaye zaman taron a kasar Habasha, inda kuma shugabannin kasashen suka hadu domin tattauna hanyoyin magance rikice rikice a Nahiyar tare da inganta huldar cinikayya.

Shugaban kasar Zambia Michael Sata, ya shaidawa manema labari cewa an gudanar da zabe tsakanin Jean Ping da Nkosazana Dlamini-Zuma amma babu wanda ya samu rinjayen kuri’u.

Sarki Farenti Elleman

Suleiman Babayo

Wannan ne taro na farko da shugabannin Afrika suka gudanar tun bayan mutuwar shugaban Libya Kanal Gaddafi wanda ke tallafawa kungiyar wanda kuma ke dasawa da kasashe masu amfani da harshen Faransanci.

A ranar Lahadi shugabannin kungiyar suka zabi shugaban kasar Jamhuriyyar Benin a matsayin sabon shugaban kungiyarsu.

Sai dai taron na kungiyar na zuwa a dai dai lokacin da ake ci gaba da samun tashe tashen hankula a kasashen kudancin Sudan da Najeriya da Somalia.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.