Mali-Nigeiya
Jami'an gwamnatin sojan Mali sun isa Nigeria don bayyana dalilin karbar mulki
Yanzu haka wata tawaga daga Sojojin da suka kwace mulki a kasar Mali na Nigeria, domin ganawa da Hukumomin na Nigeria, tare da bayyana masu musabbabin fatattakan Gwamnatin farar hula daga kasar.Jagoran ayarin, Col Blonkoro Samake ya fadawa manema labarai a Abuja cewa Shugaban Gwamnatin Sojan kasar su Mali, Amadou Sanogo ya turo su ne su 3 domin fadawa Hukumomin Nigeria halin da kasar su ke ciki.
Wallafawa ranar: