Isa ga babban shafi
Mali

Gwamnatin mulkin sojan Mali ta nemi taimakon yakan 'yan tawayen Azbinawa

Shugaban gwamnatin mulkin sojan kasar Mali, Capt Amadou Sanogo, ya nemi tallafin kasashen duniya, domin kawar da ‘yan tawayen Azbinawa na Arewaci dake ci gaba da dannawa inda suka kama garin Kidal mai mahimmanci.Kirar shugaban ya zo kwana guda, bayan kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen Afrika ta Yamma, ECOWAS-CEDEAO ta bada wa’adin kwanaki, na mayar da mulki kasar ga zababbiyar gwamnatin farar hula da aka hambarar.

Captain Amadou Sanogo
Captain Amadou Sanogo Capture d'écran de la télévision malienne.
Talla

Yayin taron manema labarai sabon shugaban Sanogo, ya nemi kawayan kasar ta Mali, su kawo dauki, domin tabbatar da iyocin kasar.

Tun cikin watan Janairu Azbiwa kasar suka zari makamai suna yakan gwamnati, domin samar da ‘yan wa yankin Azbinawa.

Juyin juya halin kasar Libya, da ya kai ga kifar da gwamnatin Magayi Shugaba Muammar Gaddafi, ya janyo yaduwar makamai cikin kasashen Afrika ta Yamma, abunda ke haddasa tashe tashen hankula a wannan yanki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.