Isa ga babban shafi
Masar

An girke tankunan yaki a fadar shugaban Masar

Rungunar Sojin kasar Masar, ta girke tankunan yaki a fadar shugaban kasa a birnin Alkahira, bayan samun wata arangama tsakanin magoya bayan Shugaba Morsi da masu zanga-zangar adawa da shi.Rahotanni daga Alkahira sun ce an samu lafawar rikicin tsakanin masu zanga-zanga bayan samun mutuwar mutane uku wasu daruruwa kuma suka rauni.

Masu Zanga Zangar adawa da Shugaban Masar Mohammed Mursi suna arangama da 'Yan Sanda
Masu Zanga Zangar adawa da Shugaban Masar Mohammed Mursi suna arangama da 'Yan Sanda REUTERS/Asmaa Waguih
Talla

Zanga-zanga dai ta barke ne a kasar Masar domin adawa da kudirin gwamnati na yi wa kundin tsarin mulki kwaskwarima.

Kuma gwamnatin kasar t ace za’a gudanar da zaben ra’ayin jama’a duk da adawa da shirin da wasu al’ummar kasar ke yi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.