Bakonmu a Yau
Malam Bello Junaidu Shugaban kula da Gidan Tarihi a Sokoto Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:17
‘Yan Tawayen kasar Afrika ta tsakiya sun amince da matakin hawa teburin sasantawa da Gwamnati tare da alkawalin dakatar da mallake biranen kasar bayan Gwamnatin ta aike da dakaru domin hana su shiga Bangui babban birnin kasar. kakakin ‘Yan Tawayen Eric Massi yace sun amince su aika da wakilansu zuwa Gabon domin tattaunawa da Gwamnatin kasar. Malam Bello Junaid Darakta a Gidan Tarihi a Sokoto a Najeriya ya yi tsokaci game da wannan batu.