Al Bashir zai kai ziyara kudancin Sudan
Shugaban kasar Sudan Umar Hassan al Bashir ya amsa goron gayyatar zuwa Kudancin Sudan bayan kasashen biyu sun amince su koma teburin sasantawa game da yankunan masu arzikin man fetir da ke kan iyakakin kasashen biyu.
Wallafawa ranar:
A wata sanarwa daga Fadar shugaba al Bashir, kakakinsa Emad Sayed Ahmed yace shugaban ya amince ya kai ziyara kudancin Sudan bayan shugaba Salva Kiir na Sudan ta Kudu ya tuntubi shi ta wayar salula.
Sai dai babu wata rana da aka ware domin ziyarar ta al Bashir.
Shugabar hukumar Tarayyar Afrika Nkosazana Dlamini-Zuma tace suna fatar ziyarar al Bashir ta kasance hanyar kawo karshen rikicin da ke tsakanin kasashen biyu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu