Isa ga babban shafi
Mali-Chadi

Keita na Mali ya kai ziyara Chadi

Zababben shugaban kasar Mali Ibrahim Boubacar Keita na gudanar da ziyarar aiki ta farko a wata kasa ta waje inda ya ziyarci kasar Chadi tare da ganawa da shugaban kasar Idris Deby a wani gari da ke gabashin kasar. Ibrahim Boubakar Keita wanda ake shirin rantsarwa a ranar 4 ga watan satumba, ya ce ya je kasar Chadi ne domin bayyana godiyarsa dangane da irin rawar da ta taka wajen ‘yantar da Mali daga hannun ‘yan tawaye da suka kwace yankin Arewaci.

Zababben shugaban kasar Mali, Ibrahim Boubacar Keïta
Zababben shugaban kasar Mali, Ibrahim Boubacar Keïta REUTERS/Joe Penney
Talla

Kasar Chadi ce ta fi kowace kasa yawan asarar sojoji a yakin Mali, wadanda ked a kwarewar yaki a sahara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.