Isa ga babban shafi
Libya

Firaministan Libya ya yi murabus

Firaministan Libya Abdallah al-Thani ya yi murabus a ranar Lahadi, bayan an kai masa hari da iyalansa, kuma matakin na zuwa ne kafin ya kafa sabuwar gwamnati bayan Majalisa ta tube Ali Zeidan da aka zarga da gazawa wajen samar da cikakken tsaro a kasar.

Firaministan Libya mai murabus Abdullah al-Thani
Firaministan Libya mai murabus Abdullah al-Thani REUTERS/Ismail Zitouny
Talla

A cikin sanarwar, al Thani yace ba zai amince da mukamin Firaministan ba saboda barazana ga rayuwar shi.

Thani wanda Ministan tsaro ne, a ranar Talatar makon jiya ne aka zabe a matsayin Firaministan bayan majalisa ta tube Ali Zeidan.

A ranar Assabar ne ‘Yan bindiga suka kai wa Firaministan hari a garin Tripoli kan hanya, amma rahotanni sun ce harin bai haifar da wani ta’adi ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.