Algeria
'Yan adawa sun kauracewa bikin rantsar da Bouteflika
'Yan adawar kasar Algeria sun ce ba zasu halarci bikin rantsar da shugaban kasar Abdelaziz Bouteflika da za'a yi yau Litinin a birnin Algeirs ba bayan sake zabensa a wa'adi na hudu yana cikin hali na rashin lafiya.
Wallafawa ranar:
Talla
Shugaban jami'yu biyar da suka kauracewa zaben, sun bukaci magoya bayansu su kauracewa bikin. Babban mai adawa da Shugaban Abderazak Mokri, yace ba su ga abin da shugaban mai fama da rashin lafiya zai yi wa kasar ba, lura da halin da ya ke ciki.
Bouteflika ya lashe zaben ne da kashi 74 abinda ya bashi damar sake rike kasar a karo na hudu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu