Isa ga babban shafi
Masar

Kotun Masar ta yanke wa magoya bayan Morsi 54 hukunci

Wata kotu a kasar Masar ta yankewa wasu magoya bayan hambararren shugaban kasar Mohammed Morsi su 54 hukuncin daurin rai rai a gidan yari. An yankewa mutanen wannan hukuncin ne, bayan da kotun ta same su da laifukan yin mu’amulla da kungiyoyin ‘yan ta’adda da aikata kisan kai da kuma tayar da tarzoma.

Magoya bayan Muhammad Morsi a Masar
Magoya bayan Muhammad Morsi a Masar REUTERS/Amr Abdallah Dalsh
Talla

Akwai kuma wasu mutane 104 da Kotun ta yanke wa hukuncin dauri tsakanin shekara daya zuwa 10 kuma cikinsu har da wasu mata daliban Makaranta guda uku.

Tun bayan hambarar da gwamnatin Mohammed Morsi na Jam’iyyar ‘Yan Uwa musulmi ake yankewa magoya bayanta hukunci tare da haramta ayyukan Jam’iyyar a Masar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.