Isa ga babban shafi
Najeriya

Ana tattauna matsalar tsaron Najeriya a Afirka ta Kudu

Shugabannin kasashen Afirka da ke halartar bikin rantsar da Jacob Zuma domin ci gaba da shugabancin kasar Afrika ta Kudu, a yau asabar suna gudanar da wani taro na musamman kan matsalar tsaro da ta dabaibaye Najeriya.

Masu zanga-zangar a sako 'yan matan Chibok
Masu zanga-zangar a sako 'yan matan Chibok REUTERS/Akintunde Akinleye
Talla

Kakakin gwamnatin Afirka ta Kudu Clayson Monyela, ya ce akwai shugabannin kasashen fiye da 20 da ke halartar bukukuwan rantsar da Zuma, kuma ko shakka babu za su halarci wannan taro domin duba yadda za a taimaka wa Najeriya fita daga cikin matsalar tsaron da take fama da ita.

A lokacin da ya shiga zauren da ake rantsar da Zuma, shugaban Najeriya Goodluck Jonathan, an tarbe shi ne ta taken Bring Back Our Girls, wato a dawo da ‘yan matan Chibok da aka sace.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.