Shugaban Bankin Duniya Jim Yong Kim ya ce rashin daidaito a tsakanin masu arziki da matalauta na daga cikin dalilan da suka sa aka kasa shawo kan cutar Ebola. Jim wanda ke gabatar da jawabi a jami’ar Howard da ke Amurka, ya ce akwai bukatar da daukar matakai domin shawo kan cutar
Cutar Ebola dai ta yita hallaka mutane daga kassahe da daman a Nahiyar Afruka ta yamma, ciki hadda kasashen Guinea da Liberiya da Najeriya da dai sauransu.
A bayan nan kuma Hukumar Lafiya ta majalisar dunkin Duniya ta bayyana cewar mai yuwa ne a farkon shekara mai kamawa ne, za’a fara amfani da Cutar Ebola a matsayin na farko da aka fara amfani da shi a Duniya, bayan da masana harhada magunguna suka kwashe Makwanni suna bincike akan Cutar da ke saurin hallaka dan Adam.
Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Malam Sani Inuwa Adam na makarantar koyar da ilimin shari’a da ke Kano kan wannan batu, ga kuma yadda zantawarsu ta kasance.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu