Isa ga babban shafi
Kenya

Kenya ta ayyana zaman makoki akan harin Jami’a

Gwamnatin kasar Kenya ta ayyana kwanakin makoki akan harin da Mayakan kungiyar al-Shebab suka kai wa Jami’ar Garissa a makon jiya abinda ya yi sanadin mutuwar Dalibai da dama

Le président Uhuru Kenyatta et son vice-président William Ruto, le 4 avril 2015 à Nairobi.
Le président Uhuru Kenyatta et son vice-président William Ruto, le 4 avril 2015 à Nairobi. REUTERS/Thomas Mukoya
Talla

Akalla dai Dalibai 148 ne suka mutu a harin mamayar da Kungiyar ta ka iwa Jami’ar har na tsawo Awa 15.

Shugaban kasra Kenya Uhuru kenyatta kuma ya bayyana cewar yanzu haka an yiwa maharan Kofar-Rago a cikin kasar inda yanzu haka ake tsare da wasu mutum 5 da ake zargi da Hannu a ciki.

Hudu daga cikin wadanda ake zargin dai ‘yan kasar Kenya ne, a yayin da na 5 daga cikinsu kuma dan kasra Tanzaniya ne, a yayin da babban wanda ake zargin ya hau kafafuwansa.

Shugaban kasar kenya Uhuru kenyatta ya bukaci al’ummar musulmin Kenya da yace suna da halayen kirki da su taimaka a gano sauran maharan da suka gudanar da wannan danyen aiki.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.