Isa ga babban shafi
EBOLA-GUINEE-SALIYO

Ana ci gaba da samun karuwar masu kamuwa da cutar Ebola a Saliyo da Guinee

Hukumar Lafiyata Majalisar Dinkin Duniya tace an samu karuwar masu kamuwa da cutar Ebola a kasashen Guinea da Saliyo a cikin makwanni biyu da suka gabata.

Wani mai aikin sa kai a laberiya na awon gano cutar Ebola
Wani mai aikin sa kai a laberiya na awon gano cutar Ebola REUTERS/James Giahyue
Talla

Hukumar tace daga ranar 7 ga wannan wata na Yuni da muke ciki an samu mutane 16 da suka kamu da cutar a yayin da wasu 15 suka kamu a kasar Saliyo.

Cutar Ebola dai ta yi sanadiyar mutuwar mutane 11,158 daga cikin mutane 27,237 da suka kamu da ita a kasashen dake yankin yammacin Afrika.

Duk da cewa yawan masu rasa rayukansu sakamakon kamuwa da ita wannan mummunar cuta ya rago a kasashen Guine Laberiya da Saliyo, har yanzu barazanar na nan bata gushe ba, ganin yadda cutar mai kisa ke da saurin yaduwa tsakanin bani Adam.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.