Isa ga babban shafi
Somalia

Al Shebab za ta fadada hare harenta a gabashin Afrika

Shugaban Mayakan Al Shebab na Somalia ya yi barazanar kaddamar hare hare a kasashen gabashin Afrika a cikin wani sakonsa na Sallah da ya aiko a shafin Intanet a yau Juma’a.

Mayakan al-Shebab na Somalia
Mayakan al-Shebab na Somalia KENYA-SECURITY/SOMALIA REUTERS/Feisal Omar/Files
Talla

Kwamandan mayakan na Al Shabaab da ake kira Ahmed Umar Abu Ubaidah, ya ambaci kasashen gabashin Afrika da suka hada da Kenya da Habasha da Djibouti da kuma Uganda.

A cikin sakon, shugaban kungiyar ya ce ba zasu dai na kai hare hare a Kenya ba musamman saboda ‘yan uwansu da kasar ke yi wa mulkin mallaka.

Ya kuma yaba da mummunan harin da aka kai a Jami’ar garin Garissa a yankin arewa maso gabashin Kenya inda mayakan Shabaab suka bindige mutane 148.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.