An kashe mayakan al-Shebab da dama a Somalia
Mayakan kungiyar Al-shebab da dama ne aka kashe a cikin wani harin jiragen sama da na makaman atilare da aka kai masu a yankin kudancin kasar Somalia, kamar yadda mahukuntan kasar kenya da ke fama da hare-haren 'yan kungiyar suka sanar.
Wallafawa ranar:
Ofisoshin Ministocin kasar Kenya 2 ne suka sanar da hare-haren da a cikinsu suka bayyana mutuwar 'yan kungiyar ta Al-shebab da dama.
Ofishin ministan cikin gidan kasar ya ce 'yan tawayen 30 suka mutu a yayin da ma’aikatar tsaron kasar ta Kenya ta ce dakarun rundunar kasashen Afrika a somalia sun kashe 'yan al-shebab 50.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu