Isa ga babban shafi
Cote D’Ivoire

Jam’iyyun adawa sun yi barazanar hana zabe a Cote D’Ivoire

Jam’iyyun adawa a kasar Cote D’Ivoire sun yi barazanar hana gudanar da zaben shugabancin kasar a ranar 25 ga watan okotba bai zuwa, matukar dai shugaba Alassane Ouattara ya ki zama da su domin warware wasu matsaloli kafin zaben.

Shugaban kasar Cote d'Ivoir Alassane Ouattara
Shugaban kasar Cote d'Ivoir Alassane Ouattara REUTERS/Luc Gnago
Talla

Jam’iyyun adawa 20 karkashin jagorancin tsohon firaministan kasar Charles Konan Banny, sun ce suna da shakku a game da batun tsaro da yakin neman zabe da kuma ita kan ta hukumar zaben kasar.

A jiya litinin aka fitar da jeren sunayen mutane 33 da ke neman takarar kujeran shugabancin kasar, wanda 3 daga cikinsu mata ne.

Kasar Cote d'voir ta fada cikin rikici da rashin zaman lafiya a shekarar 2010 bayan kammala zaben da tsohon shugaban kasar Laurent Gbabgo ya ki mika ragamar Mulkin kasar bayan ya sha kaye.

A cikin watan Afrilu Shekarar 2011 dakarun da ke biyaya ga Ouattara wanda ya yi nasara a zaben da taimakon Majalisar dinkin duniya da kasar Faransa suka tube Gbabgo daga Mulki.

Ouattara dai ya yi alkawarin gudanar da sahihin zabe a cikin kwanciyar hankali.

Sai dai ko a watan Yuni da ya gabata Dubun-dubatan Al'ummar kasar ne suka gudanar da zanga-zanga a birnin Abidjan kan nuna rashin jindadin su da mulkin Alassane Ouattara da suka ce bai tabuka abin a zo a gani ba a kasar da yaki ya tagayara.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.