Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Demokradiyar Congo

An Kashe sojojin Jamhuriyar Congo a Kivu

Wasu ‘Yan bindiga da ake zargin ‘Yan Tawayen Hutu ne sun harbe sojojin Jamhuriyar Demokradiyar Congo guda 6 har lahira a wani harin da suka kai kan iyakar kasar da ke Arewacin Kivu.

Sojojin Jamhuriyar Congo dake aiki samar da tsaro a yankin Kivu
Sojojin Jamhuriyar Congo dake aiki samar da tsaro a yankin Kivu MONUSCO/Abel Kavanagh
Talla

Justin Mukanya, shugaban mulkin Yankin, yace an yiwa sojojin kwantar bauna ne a cikin motar su inda aka hallaka su.

Yankin Rutshuru na daga cikin yankunan da yan tawayen ke aika-aika.

Wani ma'aikacin leken asirin kasar da ke Goma wanda ya tabbatar da harin ya ce maharan sun yi amfani da rokoki wajen farwa dakarun a yankin kasar da ke iyaka da Uganda da Rwanda.

Shugaban kasar Joseph Kabila na fuskantar matsin lamba kasashen duniya wajen kawo karshan rashin zaman lafiya a kasar da kuma mukushe 'yan bindiga FDLR da ke haifar da rashin zaman lafiya a arewacin da kudancin Kivu, wanda ya tilastawa mutane da dama tserewa muhallinsu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.