Isa ga babban shafi
Guinee

Shugaba Alpha Konde na kasar Guinee Conakry, ya lashe zaben shugabancin kasar

Shugaban kasar Guinne Alpha Condé ya samu rinjayen da ake bukata a zagayen farko na zaben shugabancin kasar na ranar lahadin da ta gabata, kamar yadda sakamakon wucin gadi da hukuma zaben kasar ta bayyar ya nunar.

Hoton shugaban kasar Guinee mai barin gado Alpha Condé, a Conakry.
Hoton shugaban kasar Guinee mai barin gado Alpha Condé, a Conakry. REUTERS/Luc Gnago
Talla

Tuni dai yan adawa suka sa kafa suka yi fatali da sakamakon, tare da lasar takobin yin fito na fito da shi, ta hanyar shara’a da kuma zanga zanga kan tituna

Masu lura da al’amurran siyasar kasar sun bayyan matukar damuwarsu, kan fargabar ballewar tashe tashen hankulla sakamakon ayyana daya daga cikin bangarorin biyu da ya lashe zaben.

Sakamakon wucin gadin da hukumar zaben kasar CENI ta bayar a jiya juma’a, ya tabbatar da nasara ga shugaban kasar mai barin gado Alpha Konde da yawan kuri’u miliyan 2,2 a zaben da ya samu halartar kimanin kashi 92 % na masu zaben miliyan 6 dake kan kundin zaben kasar

Sakamakon wucin gadin da hukumar zaben kasar ta bayar dai, ya fito ne daga kashi 66 % na wadanda suka halarci zaben, wanda hakan ke nufin shugaba Konde da lashe zaben shugabancin kasar tun daga zagayen farko
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.