Sojojin Chadi sun kashe mayakan Boko Haram
Gwamantin Chadi ta bayyana cewa Sojojinta sun fatattaki mayakan Boko Haram tare da kashe 14 daga cikin su bayan sun kaddamar da hare hare kan Sojojin a kusa da tafkin Chadi.
Wallafawa ranar:
Wata sanarwa da gwamantin kasar ta fitar ta ce, daya daga cikin mayakan na Boko Haram ya tarwatsa kansa tare da jikkata fararan hula 11 bayan ya tayar da bam din da ya ke dauke da shi a jikinsa.
A ranar 10 ga watan jiya ne wasu jerin hare hare uku suka kashe mutane 41 a Baga Sola da ke kusa da tafkin na Chadi, inda dubban ‘Yan Najeriya da Chadi ke samun mafaka bayan sun kauracewa gidajensu saboda rikicin Boko Haram.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu