Isa ga babban shafi
Sudan ta kudu

Sabon rikici ya kuno kai a Sudan ta Kudu

A yau Talata sabon rikici ya barke a Sudan ta Kudu, bayan wasu ‘yan bindiga sun bude wuta a wani yanki da ke yammacin kasar, batun da a yanzu ya fara haifar da furgaba sake komawa kasar gidan jiya, na rashin zaman lafiya duk da yarjejeniyar zaman lafiya da ka cimma watanni baya.

Shugaban kasar Sudan Salva Kiir da Riek Machar
Shugaban kasar Sudan Salva Kiir da Riek Machar
Talla

Rahotanni sun ce tuni mutane yankin suka fara tatara inasu, suna hijira domin tsira da ransu, al’amarin da ke zuwa a dai-dai lokacin da Majalisar Dinkin Duniya ke bayyana bukatarta na dawo da fararn hula kasar, wadanda ke hijira saboda rashin kwanciyar hankali a kasar.

Wasu kafafa yadda labaran kasar sun rawaito cewa fadan ya fara ne a yankin Yambio tsakanin Sojoji da kungiyoyi wasu matasa da ke dauke da makamai, wanda a baya aka rawaito cewa suna aiki tare ‘yan tawayen kasar da ke samun goyon bayan Riek Machar.

Rikicin da a yanzu ya fadada har zuwa yankuna kasar 3, ya sabawa sharuda yarjejeniyar zaman lafiya da gwamnatin kasar ta cimma da 'yan tawayen a watan Augustan da ya gabata, na kawo karshan yakin kasar da aka kusan shafe shekaru 2 ana fama.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.