Isa ga babban shafi
Kamaru

An kashe ‘Yan kunar bakin wake a Kamaru

Sojojin Kamaru da ‘Yan banga sun murkushe wani yunkurin kai hari da wasu ‘Yan mata biyu suka shirya kai wa a garin Kolafata da ke kan iyaka da Najeriya.

'Yan Boko Haram sun addabi yankin arewacin Kamaru
'Yan Boko Haram sun addabi yankin arewacin Kamaru AFP PHOTO/STRINGER
Talla

Jami’an tsaron sun kashe ‘Yan matan ne da ke rataye da bama bamai a jikinsu a ranar Litinin.

‘Yan banga sun harbi yar kunar bakin guda da mashi, yayin da Sojoji suka dauke guda da bindiga kafin su tayar da bom din da ke jikinsu.

Rahotanni sun ce baya ga mutuwar ‘Yan kunar bakin waken babu wani da ya mutu ko ya ji rauni.

Ana zargin ‘Yan Boko Haram ne suka yi yunkurin kai harin wadanda ke ci gaba da addabar yankin arewacin Kamaru.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.