Isa ga babban shafi
Nijar

An rufe rijistar ‘Yan takarar shugaban kasa a Nijar

Hukumar zabe a Jamhuriyar Nijar ta kammala karbar takardun ‘yan takarar da ke neman kujerar shugaban kasa a zaben da za a yi a ranar 21 ga watan Fabrairun 2016.

Tsohon Shugaban Nijar Mahamane Ousmane, da Tsohon shugaban Majalisa Hama Amadou tare da tsohon Firamnista Seini Oumarou wadanda ke hamayya da Mahamadou Issoufou a zaben 2016
Tsohon Shugaban Nijar Mahamane Ousmane, da Tsohon shugaban Majalisa Hama Amadou tare da tsohon Firamnista Seini Oumarou wadanda ke hamayya da Mahamadou Issoufou a zaben 2016 AFP via enca.com
Talla

Cikin wadanda suka gabatar da takardunsu sun hada da shugaba mai ci Mahamadou Issofou da shugaban ‘yan adawa Seyni Oumarou, da tsohon shugaban kasa Mahamane Ousmane da tsohon shugaban Majalisar dokoki Hamma Amadou wanda yanzu haka ke tsare a gidan yari.

Ma’aikatar cikin gida ne ta karbi takardun inda zata mikawa kotun tsarin mulki domin tantance ‘yan takarar kafin ranar zaben.

An shafe lokaci, Mahamadou Issoufou da Seini Oumarou da Mahamane Ousmane suna yin tasiri a siyasar Nijar.

Sauran manyan ‘yan takarar shugaban kasar sun hada da tsohon Firamnista Amadou Boubakar Cisse da tsohon Ministan noma Abdou Labo.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.