Isa ga babban shafi
MDD-Liberia

MDD ta cirewa Liberia Takunkumin Karshe

Kwamitin Sulhu na MDD ya cire takunkumai na karshe da aka kakkabawa kasar Liberia domin kawo karshen yakin basasar da ta yi fama da shi har zuwa shekara ta 2003.

Shugaba Ellen Johnson Sirleaf ta Liberia
Shugaba Ellen Johnson Sirleaf ta Liberia Reuters/Tiksa Negeri
Talla

Takunkumai na karshe da aka cirewa kasar sun shafi hanata cinikin makamai ne, sayar da ma’adinin lu’ulu’u da kuma iccen katako.

Jakaden Amurka a kasar David Pressman ya ce wannan mataki ya nuna cewa babu shaka zaman lafiya ya samu a kasar da tun shekarar 1992 take karkashin takunkumai.

Matakin na MDD zai taimakawa kasar ta fannin tattalin arzikinta, bayan shafe tsawon shekaru 13 da hana ta cinikkaya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.