Isa ga babban shafi
Israel- Ethiopia

Isra'ila Na Bukatar Kujeran 'Yar Kallo cikin Kungiyar Tarayyar Afrika

Fira Ministan kasar Habasha Hailemariam Desalegn ya bayyana goyon bayan kasar sa  ga bukatar takwaran sa na kasar Isra'ila Benjamin Netanyahu na baiwa kasar kujeran 'yar kallon cikin kungiyar Tarayyar Africa.

Fira Ministan Habasha Hailemariam Desalegn tare da bakon sa Fira Ministan Isra'ila Benjamin Netanyahu
Fira Ministan Habasha Hailemariam Desalegn tare da bakon sa Fira Ministan Isra'ila Benjamin Netanyahu REUTERS
Talla

Acewar Fira Ministan kasar Habasha,  Israila ta chanchanci matsayin saboda irin gudunmawa da take bayar wa ga kasashe da yawa a Africa.

Fira Ministan Habasha na Magana ne yayin da yake karban bakuncin Benjamin Netanyahu a birnin Addis Ababa.

Fira Ministan  Isra'ila na rangadin kasashen Africa hudu ne.

Kungiyar Tarayyar Africa kan bada gurbin zama ‘yar kallo ga kasa wadda ba cikin nahiyar Africa take ba.

A birnin Addis Ababa ake da cibiyar kungiyar Tarayyar Africa.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.