Nijar
‘Yan sanda da Dalibai na rikici akan kisan wani matashi a Maradi
Rikici ya barke a garin Maradi na Jamhuriyyar Nijar tsakanin ‘Yan sanda da daliban Jami'ar Dan Dikko Dan Kulodo bayan da wani matashi mai suna Mahamadou Isufu ya rasa ransa da aka kama a jami'ar ana tuhumarsa da satar Babur ,abin da ya kai daliban suka ma shi dukan tsiya amma bai mutu ba sai a ofishin ‘Yan Sanda, Yanzu kuma bangarorin biyu na zargin junansu da alhakin mutuwar matashin da tuni danginsa suka shigar da kara a kotu na neman hakkinsu. Wakilin mu na Maradi Salisu Issa yana dauke da rahoto.
Wallafawa ranar:
Talla
Rahoton Salissu Issa daga Maradi
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu