Isa ga babban shafi
Chad

Chadi ta kaddamar da bincike kan Kebzabo

Hukumomin Kasar Chadi sun yiwa shugaban ‘yan adawar kasar Saleh Kebzabo tambayoyi saboda zargin da ya yi na batar wasu sojojin Gwamnati 20, kwana guda bayan rantsar da shugaba Idris Deby wa’adi na biyar.

Shugaban 'yan adawar Chadi, Saleh Kebzabo.
Shugaban 'yan adawar Chadi, Saleh Kebzabo. AFP/Desirey Minkoh
Talla

Ma’aikatar shari’ar kasar tace ta kadadmar da bincike kan shugaban Yan adawar kamar yadda mai gabatar da kara ya bukata.

Ranar 28 ga watan Afrilu, kungiyar kare hakkin Bil Adama ta Human Rights Watch da Amnesty International sun yi zargin cewar sama da sojojin gwamnati 20 da wasu jami’an tsaro suka bata bayan sun ki yarda su goyi bayan takarar shugaba Idris Deby.

Kungiyoyin tare da gwamnatin Faransa sun bukaci gudanar da bincike akai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.