Isa ga babban shafi
Sudan ta Kudu

Jama'ar Sudan ta Kudu sun bukaci tura karin dakarun wanzar da zaman lafiya

Jama’a da ke gudun hijira da kuma jagororin addini a Suda ta Kudu, sun yi kira ga Majalisar Dinkin Duniya ta gaggauta tura Karin dakarun da ta yi niyyar yi zuwa kasar, saboda mawuyacin halin da mutane ke ciki.

Jami'an soji da 'yan sanda yayin sintiri a hanyoyin Sudan ta Kudu
Jami'an soji da 'yan sanda yayin sintiri a hanyoyin Sudan ta Kudu Reuters
Talla

Kiran ya zo ne yayinda gwamnatin Sudan ta Kudun, ke cigaba nuna rashin amincewa bisa tura mata Karin dakarun wanzar da zaman lafiya 4000, inda ta bayyana hakan a matsayin wani yanayi na yunkurin mamaye kasar.

Wani limamin Katolika a kasar, Ark bishop Paulino Lukudu ya ce dole ne Sudan ta Kudun ta bukaci Karin dakarun Majalisar Dinkin Duniyar, domin dawo da zaman lafiya a kasar.

A satin da ya gabata rundunar sojin Sudan ta Kudu ta sanar da cewa ta gurfanar da wasu jami'anta 60 da aka zarga da aikata laifukan yaki, da suka kunshi sata, kisan kai, da kuma azabtar da mutane.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.