Isa ga babban shafi
Somalia

Somalia ta karbi bakuncin taron Shugabanni karo na farko tun 1991

Ranar Talata kasar Somalia ta karbi bakuncin gudanar da taro na wasu daga cikin shugabannin kasashen Afrika a birnin Mogadishu, karo na farko tun bayan barkewar rikici a kasar a shekarar 1991.

Wasu daga cikin Sabbin gine gine a babban birnin Somalia, Mogadishu
Wasu daga cikin Sabbin gine gine a babban birnin Somalia, Mogadishu CC/Wikimedia
Talla

Taron ya maida hankali ne kan yadda za’a gudanar da zaben shugaban kasa dana ‘yan majalisu a kasar, sai kuma tattaunawa kan halin da kasar Sudan ta Kudu ta ke ciki.

Kasashen da suka halarci taron sun hada da Kenya, Habasha, Uganda, Djibouti, da kuma Sudan.

Kasashen dai sun cimma matsayar hada kai domin murkushe tada kayar bayan kungiyar Al-Shabaab a Somalia, da kuma farfado tattalin arzikin kasar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.