Isa ga babban shafi
Gabon

Kotu ta tabbatar da nasarar shugaba Ali Bongo

Kotun fasalta kundin tsarin mulkin kasar Gabon, ta tabbatar da nasarar shugaba Ali Bongo Ondimba, a matsayin wanda ya lashe zaben shugabancin kasar, bayan tayi watsi da bukatar ‘yan adawa na a sake kirga kuri’un da aka kada yayin gudanar da zaben.

Shugaban kasar Gabon Ali Bongo yayin zaben watan Agusta
Shugaban kasar Gabon Ali Bongo yayin zaben watan Agusta REUTERS/Gerauds Wilfried Obangome
Talla

A gefe guda kuma yayin da al’umar kasar ta Gabon ke zaman zulumi kan fargabar  barkewar rikici, gwamnatin kasar ta ce zata dora alhakin duk wani tashin hankali da ya auku, kan jagoran ‘yan adawa Jean Ping.

Tuni dai aka baza ‘yan sandan kwantar da tarzoma, a sassan titunan kasar cikin shirin ko ta kwana.

 

A baya magoya bayan jagoran 'yan adawa Jean Ping sun zargi kotun da yunkurin yi musu rashin adalci yayin yanke hukunci kan karar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.