Ping ya shigar da kara a kotu kan zaben Gabon
Dan takarar shugabancin kasar Gabon na jam’iyar adawa da ya sha kayi a zaben da aka gudanar, ya shigar da kara a gaban kotun tsarin mulki don kalubalantar sakamakon zaben da ya bai wa shugaba mai ci Ali Bongo Odimba nasara.
Wallafawa ranar:
Kotun na da makwanni biyu kafin ta yanke hukunci kan karar da Jean Ping ya shigar in da daga nan ne za ta sanar da sunan wanda ya yi nasara a zaben wanda ya haifar da cece-kuce a ciki da wajen kasar.
Tazarar kuri’u dubu sittin ne a tsakanin Ali Bongo da Ping kamar yadda sakamakon zaben na ranar 27 ga watan Augusta ya nuna.
An samu barkewar rikice-rikice a wasu biranen kasar bayan da hukuamar zabe ta sanar da sakamakon, abinda ya haddasa asarar rayuka da dama.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu