Isa ga babban shafi
Gabon

Jean Ping ya bukaci sawa Gabon takunkumi

Jagoran 'Yan adawar Gabon Jean Ping yayi kira ga kasashen duniya da su kakabawa kasar takunkumi saboda abinda ya kira magudin zaben shugaban kasar da ya baiwa Ali Bongo wa’adi na biyu.

Jagoran adawa na kasar Gabon Jean Ping.
Jagoran adawa na kasar Gabon Jean Ping.
Talla

Ping ya bukaci kasashen duniya sun sanya takunkumin kan duk wani wanda ya taka rawa wajen magudin zaben, da kuma rufe asusun ajiyar kasar dake kasashen waje kana da hana shugabannin ta tafiye tafiye.

Sabon Firaministan kasar da aka nada Emmanuel Ngondet yace a shirye yake ya kafa gwamnatin hadin kai a karshen mako, inda ya bukaci Jean Ping ya shiga tattaunawa dan dinke barakar da aka samu.

Rikicin da ya biyo bayan bayyana sakamakon zaben shugaban kasar da ya nuna Ali Bongo a matsayin wanda ya lashe zaben ya yi sanadiyar mutuwar mutane fiye da 50.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.