Kenya
Kwamishinonin hukumar zaben kasar Kenya sun yi murabus
Daukacin Kwamishinonin hukumar zaben kasar Kenya sun sauka daga mukaman su bayan an kwashe watanni a na zanga zanga a kasar saboda rashin amincewa da matsayin na su.
Wallafawa ranar:
Talla
Babban hafsa a fadar shugaban kasar, Joseph Kinyua, ya ce kwamishinonin 10 sun mika takardun su na murabus, kuma yanzu haka ta na kokarin ganin an maye gurbin su da wasu wadan da za su gudanar da zaben shekara mai zuwa.
'Yan adawa a karkashin tsohon Firaminista Raila Odinga sun zargi kwamishinonin ne da goyan bayan gwamnatin kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu