Isa ga babban shafi
Najeriya

Yaushe Buhari zai dawo Najeriya ?

Likitoci da ke diba lafiyar shugaban Najeriya Muhammadu Buhari sun ce a yau za su gudanar da gwaje gwaje akansa, inda sakamakon gwajin ne zai tantance lokacin da shugaban zai dawo.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari venturesafrica
Talla

Kamfanin dillacin labaran Reuters ya ambato wata majiya daga fadar shugaban Najeriya tana cewa Buhari ya fasa dawo wa a karshen mako, sabanin yadda aka yi hasashen zai dawo a ranar Lahadi.

Majiyar ta ce shugaba Buhari ba zai dawo gida ba domin akwai wasu gwaje-gwaje da likitoci za su yi ma sa a yau Litinin.

Ko Yaushe Buhari zai dawo ? wannan ita ce tambayar da ke bakin ‘yan Najeriya.

A watan jiya ne shugaba Buhari ya tafi London domin sake diba lafiyarsa, bayan shafe watanni biyu ba ya Najeriya a tafiyarsa ta watan Janairu.

Har yanzu dai ‘yan Najeriya ba su san irin rashin lafiyar da ke damun shugabansu ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.