Yaushe Buhari zai dawo Najeriya ?
Likitoci da ke diba lafiyar shugaban Najeriya Muhammadu Buhari sun ce a yau za su gudanar da gwaje gwaje akansa, inda sakamakon gwajin ne zai tantance lokacin da shugaban zai dawo.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Kamfanin dillacin labaran Reuters ya ambato wata majiya daga fadar shugaban Najeriya tana cewa Buhari ya fasa dawo wa a karshen mako, sabanin yadda aka yi hasashen zai dawo a ranar Lahadi.
Majiyar ta ce shugaba Buhari ba zai dawo gida ba domin akwai wasu gwaje-gwaje da likitoci za su yi ma sa a yau Litinin.
Ko Yaushe Buhari zai dawo ? wannan ita ce tambayar da ke bakin ‘yan Najeriya.
A watan jiya ne shugaba Buhari ya tafi London domin sake diba lafiyarsa, bayan shafe watanni biyu ba ya Najeriya a tafiyarsa ta watan Janairu.
Har yanzu dai ‘yan Najeriya ba su san irin rashin lafiyar da ke damun shugabansu ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu