Mata sun yi zanga-zangar sakamakon tsanantar fyade a Kano
Daruruwan matan aure da zaurawa ne suka gudanar da wata zanga-zanga a birnin Kano da ke Najeriya domin ganin nahukunta sun dauki matakai masu tsauri kan mutanen da ke yi wa mata da kanana yara fyade.
Wallafawa ranar:
Wannan dai wata babbar matsala ce da ke ci gaba yin kamari a jihar ta Kano a daidai lokacin da jama’a ke ganin cewa mahunka ba sa daukar matakan da suka dace domin magance matsalar.
Wakilinmu a Kano Abubakar Abdulkadir Dangambo, ya ce a cikin shekara daya kacal an samu rahotannin aikata fyade fiye da sau 700 a cikin jihar, lamarin da ya janyo hankalin kungiyar tsoffin daliban makarantar St-Louis shirya zang-zangar ta ranar talata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu