Isa ga babban shafi
Rwanda

Al'ummar Rwanda na bikin nasarar Kagame

Al’ummar Rwanda na gudanar da bikin murnar nasarar da shugaba Paul Kagame ya samu a zaben shugabancin kasar karo na uku, in da ya yi alkawarin ci gaba da kawo sauyi a kasar.

Shugaban Rwanda Paul Kagame tare da dimbim magoya bayansa
Shugaban Rwanda Paul Kagame tare da dimbim magoya bayansa REUTERS/Jean Bizimana
Talla

Shugaba Kagame da ya fara jagorantar Rwanda tun bayan kawo karshen kisan kare dangi a shekarar 1994, ya samu sama da kashi 98 cikin 100 na kuri’un da aka kada.

Sai dai ana zargin shugaban da yin mulkin kama-karya, amma mutanen kasar na yaba ma sa saboda rawar da ya taka wajen inganta tattalin arzikinsu.

Kimanin mutane miliyan 6 da dubu 900 ne suka fito don kada kuri’unsu, yayin da Kagame mai shekaru 59 ya shafe tsawon shekaru 17 akan karagar mulki.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.