Bakonmu a Yau
Gwamnan Adamawa ya zargi jihohi da yin sakaci kan matsalar manoma da makiyaya a Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:01
Daya daga cikin matsalolin da suka addabi Najeriya a yau ita ce matsalar rikici tsakanin makiyaya da manoma, abin da ke kai ga rasa rayuwa da kuma dimbin dukiya.Yayin da ake ci gaba da lalubo hanyar magance matsalar, gwamnan jihar Adamawa Sanata Bindow Jibrilla ya zargi gwamnonin Jihohi da sakaci har matsalar ta yi girma.Ga dai abin da ya shaida wa Bashir Ibrahim Idris a zantawar da su ka yi da shi a Lagos.