Isa ga babban shafi
Afrika ta Kudu

Ramaphosa ya yi wa Majalisar Ministocinsa garambawul

Sabon shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa, ya yi wa Majalisar Ministocin kasar garambawul kwanaki 11 bayan hawarsa karagar mulki, in da ya mayar da Nhlanhla Nene wanda Jacob Zuma ya kora a matsayin Ministan Kudi.

Sabon shugaban kasar Afrika ta kudu Cyril Ramaphosa.
Sabon shugaban kasar Afrika ta kudu Cyril Ramaphosa. AFP/Rodger Bosch
Talla

Shugaban ya kuma nada David Mabuza, Firimiyan Yankin Mpumalanga a matsayin mataimakin shugaban kasa, tare da wasu sabbin mukaman ministoci da mataimakansu 30.

Rahotanni sun ce, shugaban ya kori wasu daga cikin ministocin Zuma, yayin da ya nada tsohuwar matarsa, Nkosaza Dlamini-Zuma da suka fafata da ita wajen neman shugabancin Jam’iyyar ANC a matsayin ministar tsare-tsare a fadar shugaban kasa.

Mr. Ramaphosa ya dare kan kujerar shugabancin kasar ne bayan jam'iyyar ANC ta kori Zuma bisa zargin cin hanci da rashawa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.