'Yan Boko Haram sun kashe ma'aikatan agaji 4 a Najeriya
Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton cewa ‘yan Boko Haram ne sun kai hari tare da kashe ma’aikatan agaji hudu a karamar hukumar mulkin Kala-Balge da ke jihar Borno.
Wallafawa ranar:
Mai magana da yawun Majalisar Dinkin Duniya Samantha Newport, ta ce an kai harin ne a yammacin ranar jiya alhamis, inda aka kashe mutanen hudu da raunata daya, yayin da daya ya bata a kusa da garin Rann wanda shi ne shalkwatar karamar hukumar mulkin ta Kala-balge a jihar Borno.
Majalisar Dinkin Duniya ta ce tana fargar cewa anh yi garkuwa da jami’in daya da ya bata a wannan yanki da ya yi kaurin suna sakamakon rashin tsaro.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu