Isa ga babban shafi
Najeriya

'Yan Boko Haram sun kashe ma'aikatan agaji 4 a Najeriya

Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton cewa ‘yan Boko Haram ne sun kai hari tare da kashe ma’aikatan agaji hudu a karamar hukumar mulkin Kala-Balge da ke jihar Borno.

Jagoran Boko Haram, Abubakar Shekau
Jagoran Boko Haram, Abubakar Shekau AFP PHOTO / BOKO HARAM
Talla

Mai magana da yawun Majalisar Dinkin Duniya Samantha Newport, ta ce an kai harin ne a yammacin ranar jiya alhamis, inda aka kashe mutanen hudu da raunata daya, yayin da daya ya bata a kusa da garin Rann wanda shi ne shalkwatar karamar hukumar mulkin ta Kala-balge a jihar Borno.

 

Majalisar Dinkin Duniya ta ce tana fargar cewa anh yi garkuwa da jami’in daya da ya bata a wannan yanki da ya yi kaurin suna sakamakon rashin tsaro.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.