Isa ga babban shafi
Najeriya

Buhari ya gaza komawa gida kwanaki 2 bayan barin Amurka

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya gaza komawa gida kwanaki biyu bayan barinshi kasar Amurka inda ya gana da shugaban kasar Donald Trump, ganawar da ta kai ga kara dankon alakar da ke tsakanin kasashen biyu ta fuskar tsaro da kasuwanci.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari. NAN
Talla

A jiya Laraba ne dai al'ummar Najeriyar suka zuba idon isowar shugaban amma kuma kawo yanzu babu wasu bayanai kan isowar ta sa.

Sanarwar da mataimakin shugaban na musamman kan harkokin yada labarai Malam Garba Shehu ya fitar ta ce yanzu haka shugaban na birnin London yayin da ya gaza tasowa saboda wasu matsaloli.

Tun farko dai fadar shugaban kasar ba ta sanar da cewa Muhammadu Buhari zai tsaya a birnin London bayan ganawa da Donald Trump a Amurka ba.

Bayan ganawa da Trump a ranar 29 ga watan Aprilu ne Muhammadu Buhari ya bar Washington ranar 1 ga watan Mayu inda guda daga cikin mataimakanshi kan harkokin yada labrai Bashir Ahmad ya ce shugaban na kan hanyar shi ta dawowa Najeriya, amma kuma kawo yanzu bayanai na nuni da cewa jirgin shugaban na birnin London.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.