Fararen fata za su tsunduma yajin aiki a Afrika ta kudu
Dubban fararen fata ma’aikatan kamfanin ma’adinai na Sasol da ke Afrika ta kudu sun shirya tsunduma yajin aikin sai baba ta gani a gobe litinin bayan wani shirin gwamnatin kasar na yin raba dai-dai tsakanin fararen fatar kamfanin da bakaken fata ta fuskar kadadrorin da suka mallaka.
Wallafawa ranar:
Matakin wanda gwamnatin ta gabatar karkashin shirinta na bunkasa tattalin arzikin bakaken fata, ta nemi ilahirin kamfanonin kasar su cimma daidaito kan yadda za a yi raba dai dai na mamallakansu tsakanin bangaren fararen fata da bakake, wanda ke da nufin kawo karshen takaddamar dimbin shekaru da ke tsakaninsu.
Sanarwar da kungiyar kwadago bangaren fararen fata a kamfanin na Sasol ta fitar ta ce ma’aikatanta fiye da dubu 6 da dari 3 da ke kamfanin za su tsunduma yajin aikin a gobe Litinin.
Kamfanin Sasol wanda ya yi kaurin suna ta fannin kimiyyar mayar da gawayi da Iskar gas zuwa man fetur a bara ne yasha alwashin raba dai dai kan nau’in mutanen da suka mallaki sassanshi tsakanin fararen fata da bakake.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu