Isa ga babban shafi
Afrika ta Kudu

Fararen fata za su tsunduma yajin aiki a Afrika ta kudu

Dubban fararen fata ma’aikatan kamfanin ma’adinai na Sasol da ke Afrika ta kudu sun shirya tsunduma yajin aikin sai baba ta gani a gobe litinin bayan wani shirin gwamnatin kasar na yin raba dai-dai tsakanin fararen fatar kamfanin da bakaken fata ta fuskar kadadrorin da suka mallaka.

Shugabanci karkashin Cyril Ramaphosa a Afrika ta kudu na da nufin samar da daidaito tsakanin bakaken fata da farare wadanda ke rike da kaso mai yawa na arzikin kasar.
Shugabanci karkashin Cyril Ramaphosa a Afrika ta kudu na da nufin samar da daidaito tsakanin bakaken fata da farare wadanda ke rike da kaso mai yawa na arzikin kasar. Themba Hadebe / POOL / AFP
Talla

Matakin wanda gwamnatin ta gabatar karkashin shirinta na bunkasa tattalin arzikin bakaken fata, ta nemi ilahirin kamfanonin kasar su cimma daidaito kan yadda za a yi raba dai dai na mamallakansu tsakanin bangaren fararen fata da bakake, wanda ke da nufin kawo karshen takaddamar dimbin shekaru da ke tsakaninsu.

Sanarwar da kungiyar kwadago bangaren fararen fata a kamfanin na Sasol ta fitar ta ce ma’aikatanta fiye da dubu 6 da dari 3 da ke kamfanin za su tsunduma yajin aikin a gobe Litinin.

Kamfanin Sasol wanda ya yi kaurin suna ta fannin kimiyyar mayar da gawayi da Iskar gas zuwa man fetur a bara ne yasha alwashin raba dai dai kan nau’in mutanen da suka mallaki sassanshi tsakanin fararen fata da bakake.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.