Isa ga babban shafi
Faransa-Mali

Dakarun Faransa a Mali sun kashe mayakan jihadi

Rundunar Faransa a kasar Mali ta sanar da kai wasu samame kan ayarin wasu mayakan jihadi a arewacin kasar daga daren Alhamis zuwa jiya juma’a.Sanarwar da Minstar tsaron Faransa Florence Parly ta sanyawa hannu tareda bayyana cewa Faransa ta yi amfani da manyan jiragen yaki, jirage masu saukar ungulu.

Wasu daga cikin jiragen yakin kasar Mali
Wasu daga cikin jiragen yakin kasar Mali © FAMA
Talla

Samamen da Dakarun Faransa suka kai ya kai su ga samun nasarar murkushe mayakan jihadi da dama, daga cikin su ana yi zana Hamadoun Kouffa mataimakin daya daga cikin Shugabanin kungiyoyin yan tawayen arewacin Mali Iyag Ag Ghali .

Akalla Faransa ta girke kusan soji 4.500 a yankin Sahel, rundunar dake taimakawa wajen yaki da yan ta’ada a yankin na Sahel.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.