Ghana-Najeriya
Martanin Najeriya dangane da korar da Ghana ta yiwa wasu yan kasar
Jakadan Nigeria a Ghana Michael Abikoye ya nuna rashin jin dadin Najeriya game da korar ‘yan Najeriya 723 da Ghana tayi tsakanin shekarar da ta gabata zuwa wannan lokaci.
Wallafawa ranar:
Talla
Jakadan Nigeria a Ghana Michael Abikoye ya
fadawa wani taro da yayi da jami’an hukumar kula da shige da fice na Ghana cewa abin babu dadi ko kadan.
Ya ce ‘yan Nigeria 81 aka kora a watan jiya saboda zargin zanba ta yanar gizo da zarce wa’adin zama a kasar, yayinda a wannan watan aka kori mutane 115 saboda zargin karuwanci da kuma zarce wa’adin zama a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu